Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Mutane da dama sun rasa ransu a sabon rikicin kabilanci a jihar Filato

Published

on

Mutane da dama ne a ka kashe a wani sabon rikicin kabilanci daya barke a Yelwan Zangam, dake karamar hukumar Jos ta Arewa, a jihar Plateau.

Rahotanni sun tabbatar dacewar an kona gidaje da dama, a sabon rikicin da ya barke a ranar 24 ga Agusta, mako daya bayan kashe wasu Fulani matafiya su 27, a Gada Biyu zuwa Rukuba, ta jihar.

Wani shaidar gani da ido ya shaidawa jaridar Daily Trust, cewar sama da mutane talatin ne aka kashe a sabon rikicin.

Rikicin ya biyo bayan gargadin da rundunar sojin kasar nan, ta ‘Operation Safe Haven’ mai kokarin wanzar da zaman lafiya a jihohin, Bauchi da Kaduna, tayi na cewar wasu daga cikin bata gari na kokarin sake kitsawa tare da tayar da rikici a jihar ta Plateau.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!