Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Mutane na da ‘yancin daukar hoto ko bidiyon ‘yan sanda yayin gudanar da aiki

Published

on

Hukumar ‘yan sandan Najeriya ta ce yan ƙasar na da damar ɗaukar bidiyo da hotunan ‘yan sanda a lokacin da suke gudanar da aiki.

 

Mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan ƙasar, Muyiwa Adejobi ne ya bayyana haka cikin wata sanarwa da ya fitar a shafinsa na X ranar Alhamis.

 

Adejobi na mayar da martani ne kan saƙon da wani mai amfani da shafin ya wallafa da ya ce ‘yan sanda sun tatse shi naira 10,000 saboda bidiyon da ya ɗauke su a lokaci da suke binciken ababen hawa.

 

Kakakin rundunar ya ce ba laifi ba ne ɗaukar hoto da bidiyon ‘yan sanda a lokacin da suke bakin aiki.

 

Ya ƙara da cewa rundunar ta sha gaya wa mutanen cewa babu laifi ɗaukar bidiyo da hotunan ‘yan sandan da ke bakin aikin.

 

Mista Adejobi ya ce duk wanda ‘yan sanda suka ci zarafinsa saboda ɗaukarsu bidiyo ko hoto su kai rahoto ga hukumar ‘yan sanda.

 

Cikin sakonsa na X da ya wallafa, mista Adejobi ya ce ”ya kama kowane ɗan sanda ya sani cewa ba laifi ba ne ɗaukar bidiyo ko hotunansu a lokacin da suke bakin aiki”.

 

“Waɗanda ke cin zarafin masu ɗaukarsu hoto ko bidiyo saboda wannan, su daina”.

 

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!