Connect with us

Labarai

Mutum 1 ya rasu sakamakon ruftowar gini a Kirikasamma

Published

on

 

Majalisar ƙaramar hukumar Kirikasamma ta jihar Jigawa ta tabbatar da mutuwar mutum ɗaya da kuma jikkatar wasu bakwai sakamakon rushewar wani gini a yankin.

 

Jami’in yaɗa labaran hukumar, Musa Muhammad, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar ga manema labarai.

 

Ya ce lamarin ya faru ne bayan ruwan sama mai yawa da aka samu a Kirikasamma da kewaye, inda ginin ya rushe a ƙauyen Kabak da tsakar dare ranar juma’a.

 

Muhammad ya bayyana cewa mutum bakwai sun jikkata sosai, yayin da mutum ɗaya ya rasa ransa.

 

Cikin waɗanda suka jikkata, biyar an kwantar da su a asibiti don samun kulawa, yayin da aka sallami sauran biyu bayan samun magani.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!