Connect with us

Ƙetare

Mutum 16 sun mutu yayin da 400 suka jikkata a zanga-zangar Kenya

Published

on

Rahotanni sun bayyana cewa mutane 16 sun mutu, yayin da 400 kuma suka jikkata, inda jami’an tsaro suka kama karin matasa 61 a zanga-zangar da aka gudanar a faɗin kasar Kenya jiya Laraba, domin tunawa da shekara daya da zanga-zangar adawa da ta biyo bayan ƙarin haraji da gwamnatin ƙasar ta yi, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane da dama.

 

Hukumar kare haƙƙin Dan-adam ta ƙasar KNCHR ta ce, ta tabbatar da mutuwar mutum 8 da harbin bindiga ya kashe su a wuraren da suka hada da Machakos da Makueni da Kiambu sai Nakuru da kuma Nyandarua.

 

Sai dai Kamfanin dillancin labarai na Reuters, ya bayyana cewa Amnesty Kenya ta ce, mutum 16 ne suka mutu.

 

An samu hargitsi da tarzoma a wurare da dama, ciki har da toshe hanyoyi tare da yin jifa da Duwatsu da amfani da hayaki mai sa hawaye da ruwa zafi da kuma yunkurin mamaye Majalisar dokokin ƙasar.

BBC ta ruwaito cewa, hukumar sadarwa dai ta hana yada shirye-shirye kai tsaye, amma gidajen rediyo da talabijin sun ƙi bin umarnin, inda suka ci gaba da yada zanga-zangar a kafafensu na sada zumunta.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!