Connect with us

Labarai

Mutume 176 sun mutu sakamakon cutar zazzaɓin Lassa- NCDC

Published

on

Hukumar kula tare da dakile cutuka masu yaduwa ta Najeriya NCDC, ta tabbatar da mutuwar mutume 176 sakamakon cutar zazzaɓin Lassa a jihohi 21 cikin watanni 10.

NCDC ta ce adadin mutanen da cutar ke kashewa ya ƙaru daga kashi 16.6 cikin 100 a 2024 zuwa 18.4 a 2025 duk da raguwar masu kamuwa da cutar a tsakanin.

Hukumar ta ɗora alhakin mutuwar kan rashin kai rahoto da wuri, da rashin neman taimakaon likitoci.

Haka kuma, hukumar ta bayyana cewa, ƙarin mutane 955 ne daga cikin 8,367 da aka gwada suka kamu da cutar ta Lassa a 2025, inda jihohin Ondo, Bauchi, Edo, Taraba suka zama cibiyar cutar da kashi 88 cikin 100 na duka mutanen.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!