Connect with us

Labarai

NAFDAC ta kama dan wasan kwallon kafa bisa zarginsa da raba wa mutane kayan maye

Published

on

Hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta Najeriya NAFDAC, ta kama wani dan wasan kwallon kafa mai suna Mista Ikechukwu Elijah a unguwar Apo-Waru da ke birnin tarayya Abuja bisa laifin rarraba sinadarai masu hadari ga mutane.

 

Hakan na cikin wata sanarwa  mai dauke da sa hannun mataimakin daraktan hulda da jama’a na hukumar Mista Adegboyega Osiyemi, da ya fitar a safiyar yau Juma’a.

 

A cewar sanarwar, ta NAFDAC ta ce wanda ake zargin yana gudanar da wata haramtacciyar masana’anta ne a cikin wani gida da ke yankin, kuma ya yi kaurin suna wajen yin jabun wasu nau’in sinadarai  da ka iya cutar da rayuwar al’ummar kasar nan

 

Hukumar NAFDAC ta sha yin gargadin cewa irin wadannan abubuwa na sanya ‘yan kasa su shiga cikin abubuwa masu hadari, baya ga barazana ga harkokin tsaro a kasa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!