Labarai
NAHCON ta sha alwashin fara shirye-shiryen aikin Hajjin bana a kan lokaci

Hukumar Kula da Aikin Hajji ta Najeriya NAHCON ta jaddada kudirinta na fara shirye-shiryen aikin Hajjin shekarar 2026 a kan lokaci.
Shugaban hukumar, Farfesa Abdullahi Saleh Usman, ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa da Mai taimaka masa na Musamman kan Harkokin Yaɗa Labarai, Ahmad Mu’azu, ya fitar a daren jiya Lahadi a Abuja.
Ya ce, hukumar na aiki daidai da manufofin Gwamnatin Tarayya ƙarƙashin jagorancin Shugaba Bola Ahmed Tinubu,
Haka kuma, ya kara da cewa, Shugaban NAHCON ya kuma amince da tura babbar tawagar shugabanni zuwa Masarautar Saudiyya, domin kammala da karɓar dukkan shirye-shiryen masauki da suka rage a Makkah, tare da kauce wa duk wata tangarda a aiki.
You must be logged in to post a comment Login