Connect with us

Labarai

Najeriya na fuskantar karin matsalar yunwa cikin shekaru 10 – WFP

Published

on

Hukumar Abinci ta Majalisar Ɗinkin Duniya (WFP) ta yi gargaɗin cewa Nijeriya na fuskantar yunwa mafi tsanani cikin kusan shekara goma, yayin da rage tallafin agaji ke ƙara tsananta matsalar rashin abinci mai gina jiki a yankin Arewa maso Gabas.

A cewar WFP, a Jihar Borno kaɗai, kusan mutane 15,000 na fuskantar barazanar ƙarancin abinci mai tsanani, yayin da ake hasashen fiye da yara miliyan 13 a Arewa maso Gabas za su kamu da matsalar rashin abinci mai gina jiki a bana.

Hukumar ta ce rikice-rikice, gudun hijira da matsin tattalin arziki sun daɗe suna haddasa matsalar ƙarancin abinci, amma rage tallafin agaji yanzu ya kai al’umma masu rauni matakin da ba za su iya jurewa ba.

Mataimakiyar daraktar WFP na yankin Yammaci da Tsakiyar Afirka, Sarah Longford, ta ce raguwar kuɗaɗen tallafi da aka samu a shekarar 2025 ya ƙara tsananta yunwa da rashin abinci mai gina jiki a fadin yankin Arewa maso Gabas.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!