Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Tsaro: dubunnan mutane na fuskantar barazanar yunwa a Nijar

Published

on

Sama da mutane dubu 600 ne, ke fuskantar barazanar fadawa cikin matsalar karancin abinci a jihar Tillaberi dake yammacin jamhuriyyar Nijar.
Hukumar Majalisar Dinkin Duniya mai kula da kai tallafin jin kai OCHA reshen ƙasar ce ta bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ta fitar.

Rahoton ya bayyana cewa yawan samun hare-haren ƴan bindiga kan manoma ne ya sanya yunwa musamman a yankin Anzourmawa
Magajin garin ƙaramar hukumar Sare kwara, Malam Hadi Djibo ya tabbatarwa da Freedom Radio cewa, a baya bayannan ƴan bindiga sun kashe mutane uku a gonakin su.

Hukumar ta OCHA ta kuma bayyana cewa, bayaga barazanar rashin tsaro, janyewar ruwan sama da wuri a yankin Tilleberi ya sanya ƙarin samun ƙarancin abinci

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!