Connect with us

Labarai

Najeriya za ta koma kan tsarin e-Visa a watan Mayu- Minista

Published

on

Gwamnatin tarayya, ta ce, za ta myar da harkokin Biza zuwa kafar Internet watau e-Visa daga ranar 1 ga watan Mayu.

Ministan harkokin cikin gida na kasar nan Tunji Ojo da takwaransa na bunkasa harkokin sufurin jiragen sama Festus Keyamo, ne suka bayyana hakan jiya laraba a birnin tarayya Abuja yayin taron dabbaka sabon tsarin a ayyukan hukumar lura da shige da fice ta kasa.

Sabuwar fasahar dai za ta bai wa masu shigowa kasar nan damar neman Biza ta Internet ba sai sun je ofishin jakadanci ba, inda hakan zai saukaka wa matafiya.

Haka kuma sun kara da cewa, a wannan sabon tsaro masu bukatar Biza za su cike dukkan bayanai ne tare da biyan kudin neman Bizar inda kuma bayan cika ka’idoji za a tura musu da Bizar ta sakon Email, kamar yadda ake yi a wasu manyan kasashen duniya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!