Connect with us

Labarai

NAPTIP ta ceto yaran da aka sace daga arewaci zuwa kudancin Najeriya

Published

on

Hukumar da ke yaƙi da safarar mutane a Najeriya, NAPTIP, ta ce ta ceto wasu yara takwas da ake zargin an sace su ne daga wasu jihohin arewacin ƙasar ciki har da jihar Kano.

Kakakin hukumar, Vincent Adekoye, ya ce an gano yaran ne a wani gidan marayu da ya yi suna a garin Asaba da ke jihar Delta a kudancin ƙasar.

Hukumar farin kaya ta DSS da jami’an ƴansanda da na civil defence ne suka ceto yaran a yayin wani samame da suka kai a gidan marayun.

Ƙawancen jamu’am tsaron sun kai samamen ne bayan ƙorafe-ƙorafen da iyayen yara suka kai na cewa ƴaƴansu sun ɓata a jihar Kano da wasu maƙwabtan jihohi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!