Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

NEMA zata maye gurbin motocin da rikicin shi’a ya lalata

Published

on

NEMA zata maye gurbin motocin da rikicin shi’a ya lalata

Hukumar agajin gaggawa ta kasa NEMA ta ce, zata kashe Naira milliyon dari biyu don sayen motocin daukan marasa lafiya da nufin maye gurbin wadandan suka kone a rikicin da ya auku tsakanin jami’an kasar nan da kungiyar mabiya shia a watan Yulin daya gabata.

Baban daraktan hukumar Mustapha Maihaja ne ya bayyana hakan yayin  zantawa da manema labarai.

Maihaja ya kuma ce, kawo yanzu shirye-shirye sun yi nisa na fara aiwatar sayen motocin don gudanar ayyukan su yadda ya kamata, ba tare bata lokaci ba.

Yana mai cewa, tuni gwamnatin tarraya ta amince da sayen motocin daukan marasa lafiya.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!