Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

An Tashi Lafiya

Nijar ta karɓi bashin miliyan dubu ɗari biyu da ashirin na Cefa, domin yaƙi da matsalar yunwa da kuma inganta rayuwar al’umma

Published

on

Jamhuriyar Nijar ta samu rancen kuɗi daga Bankin Duniya sama da miliyan dubu dari biyu da ashirin na Cefa, dai-dai da dalar amurka miliyan dari huɗu, domin tunkarar matsalar yinwa da inganta rayuwar al’ummar kasar.

Tuni dai wasu kungiyoyin manoma da na raya ayyukan karkara suka fara tofa albarkacin bakinsu akan samun bashin.

Shugaban ƙungiyar mutanan karkara Malam Abdu Gajango ya bayyana farin cikin sa, game da wannan ƙudiri, ya kuma ƙara da cewa, ya kamata Gwamnati ta mai da hankali a wuraren da suka fi buƙata, tare da mai da hankali akan su kansu makiyaya ta kuma guji yin “rabon ɗan kishiya.”

Ayyukan da Gwamnatin zata gudanar sun haɗa da, gina magudanan ruwa, ceto gandun daji, da kuma samar da ingantaccen ruwan sha a yankunan karkara, sai kuma samarwa da makiyaya mashayar dabbobi. Ana kuma sarai aƙalla mutane miliyan uku ne zasu ci gajiyar waɗannan ayyukan.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!