Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Buhari zai sake nazartar kasafin kudi sakamakon bullar cutar Corona

Published

on

Gwamnatin tarayya ta ce bullar cutar Corona da kuma faduwar farashin gangar danyan mai, ya sanya dole ta sake nazartar kasafin kudin wannan shekara.

Ministar kudi, kasafi da tsare-tsare Zainab Ahmed ce ta bayyana haka yayin zantawa da manema labarai a fadar shugaban kasa, bayan kammala taron majalisar zartaswa ta kasa.

Ta ce, bullar cutar ta sanya wajibi gwamnati ta sake nazartar kasafin kudin saboda ya zo mata a bazata.

Haka zalika ministar ta kuma ce, farashin gangar danyan mai ya fadi a kasuwannin duniya, inda a yanzu ake sayarwa akan dala hamsin da biyu.

Anyi kira ga shugaba Buhari da ya kawo karshen matsalar tsaro

Buhari zai yi titi daga Sokoto zuwa Nijar

Bashin da ake bin Najeriya ya ninka kasafin kudin badi-Akibu Hamisu

wanda hakan ya yi kasa da yadda aka tsara kasafin kudin kasar nan akan dala hamsin da bakwai.

Sai dai ta ce, an samu ci gaba ta bangaren hakar mai domin yanzu kasar nan tana iya fitar da ganga miliyan biyu da dubu dari daya a duk rana.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!