Connect with us

Labarai

NiMet ta yi hasashen yin Hazo da ruwan sama a wasu sassan Najeriya

Published

on

Hukumar Kula da Yanayi ta Najeriya NiMet ta yi hasashen cewa za’a samu yanayin Hazo da kuma ruwan sama a wasu sassan Najeriya nan daga yau Litinin zuwa Laraba.

Hakan na cikin wata sanarwa da hukumar ta fitar a shafinta a X.

Cikin jihohin  da hukumar ta yi hasashen za a iya fskantar wannan yanayi hadar da Borno da Zamfara da Yobe da Jigawa  da Katsina da Kaduna sai kuma Kano

Cikin wani rahoton da hukumar ta fitar ranar Lahadi ta buƙaci al umma su zama cikin shiri domin tunkarar waɗannan yanayi.

Haka ma hukumar ta ce akwai hasashen samun ruwan sama haɗe da tsawa a wasu yankunan jihohin Taraba da Adamawa.

Hukumar ta kuma yi hasashen samun rana a wasu jihohin arewa ta tsakiyar ƙasar, da kuma yiwuwar samun ruwan sama a jihohin Nasarawa da Kogi da Birnin Tarayya Abuja.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!