Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Nimet tace akwai hasashen samun mamakon ruwan sama Awasu jihohin Arewa

Published

on

Hukumar Kula da Yanayi ta kasa (NIMET) ta ankarar da wasu mazauna jihohin arewa kan su shirya wa mamakon ruwan sama a ƴan kwanaki masu zuwa.

A cewar sanarwar da aka fitar a jiya Alhamis, ana ganin gangamowar hadari a wasu sassan arewacin ƙasar nan ciki har da Borno da Taraba da Gombe da Bauchi da kuma Kano, inda ake tsammanin hadarin zai yaɗu zuwa yammacin kasar.

Sanarwar ta ƙara da cewa hadarin da ake fuskanta ana sa ran zai kai ga gabashin ƙasar haɗe da iska a jihohin Plateau da Nasrawa da Jigawa da Adamawa da Yobe da Borno da Bauchi da Gombe da Kaduna da Kano da kuma Katsina.

NIMET ta kuma ce yankunan da ake tsammanin hadari, akwai yiwuwar a yi iska mai ƙarfi da ake sammanin zai zo da ruwan sama, da ka iya lalata bishiyoyi da turakun wutar lantarki da gine-gine masu rauni.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!