Connect with us

Labarai

Nuhu Ribadu ya jagoranci tawaga ta musamman zuwa Amurka don tattaunawa

Published

on

Mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Malam Nuhu Ribadu, ya jagoranci wata tawaga ta musamman zuwa ƙasar Amurka domin tattaunawa kan zargin da wani ɗan majalisar wakilai na Amurka ke yi cewa, ana cin zarafin Kiristoci a Najeriya.

A cewar majalisar tsaron Najeriya wannan zargin na iya haifar da matsalolin fahimta tsakanin al’ummomi tare da bata sunan Najeriya a idon duniya, saboda haka gwamnatin tarayya ta ga dacewar tura tawaga ta musamman don gabatar da hujjoji da bayanai na gaskiya.

Tawagar ta yi bayanin cewa Najeriya ƙasa ce mai al’adu da addinai daban-daban wadda ke kare hakkin kowane ɗan ƙasa ba tare da nuna wariya ba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!