Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

NYSC ta sanya ranar yaye ‘yan hidimar kasa rukuni na biyu

Published

on

Hukumar kula da matasa ‘yan hidimar kasa ta sanar da cewa a ranar 16 ga watan Yulin nan da mu ke ciki ne za ta yaye matasa ‘yan hidimar kasa ‘yan rukuni na biyu.

Wannan na cikin wata sanarwa da hukumar ta fitar yau mai dauke da sa hannun daraktar yada labaranta Mrs Adenike Adeyemi, tana mai cewar za a gudanar da bikin yaye matasan ne bisa matakan kariya daga yaduwar cutar Covid-19.

Sanarwar ta kara da cewa matasan za su karbi shaidar kammala hidimar a kananan hukumomi a cikin kwanaki goma, don tabbatar da bin matakan da cibiyar dakile yaduwar cututtuka ta kasa NCDC ta gindaya na hana cunkoso.

Ta cikin sanarwar, shugaban hukumar Birgediya Janar Shu’aibu Ibrahim ya taya matasan murnar kammala hidimar, sannan ya ja hankalinsu da su ci gaba da kasancewa ‘yan kasa nagari a duk inda suka samu kansu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!