Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ofishin jakadancin Najeriya da ke kasar Jamus ya bukaci bayanai kan harin da aka kaiwa Ike Ekweremadu

Published

on

Ofishin jakadancin Najeriya da ke kasar Jamus ya bukaci hukumomi a kasar Jamus din, da su fito da bayanan wadanda aka kama da hannu wajen cin zarafin sanata Ike Ekweremadu a kasar ta jamus ranar 17 ga watan Agustan da muke ciki.

A wata sanarwa da ofishin jakandancin kasar nan ya fitar a birnin Berlin,ta ce ofishin ya kuma bukaci a hukunta masu laifin dai-dai da dokokin kasar ta Jamus.

Haka kuma Ofishin ya kuma bukaci hukumomin kasar ta jamus da su tsananta bincike don gano hakikanin masu laifin don hukunta su yadda ya dace.

Ofishin jakadancin Najeriya a kasar Jamus ya kuma ce gudanar da bincike da hukunta masu laifin zai karya gwiwar masu yunkurin yin irin hakan a nan gaba.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!