Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Oluremi Tinubu:ta bukaci da gwamnatin tarraya ta bada hutun kasa don baiwa jama’a damar karbar katin zabe

Published

on

‘Yar majalisar Dattijai mai wakiltar mazabar Lagos ta tsakiya Oluremi Tinubu ta yi kira ga gwamnatin tarayya da ta ware ranaku domin bada hutu a fadin kasar nan don al’umma su samu damar karbar katinsu na zabe na dindindin.

Oluremi Tinubu na bayyana hakan ne a jiya Lahadi a Lagos, sakamakon gabatowar wa’adin watan Disamban bana don kammala karbar katin zaben.

Wannan kira na zuwa ne a daidai lokacin da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ke cewa katunan zabe sama da miliyan bakwai ne a hannun hukumar, wanda kawo yanzu ba a karba ba.

‘Yar majalisar dattijan ta bukaci a fadada shirin rabon katin ya kai har lokacin hutun karshen mako don baiwa ma’aikata damar karbar na su katunan.

Sannan ta bukaci hukumar INEC da ta samar da duk wasu abubuwa da ake bukata domin saukaka aikin raba katin zaben na dinidindin

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!