Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Rundunar yan sanda a Akwa Ibom sun kame ma’aikatan sa idon aikin zabe na boge

Published

on

Rundunar ‘yan’sanda jihar Akwa Ibom ta ce ta samu nasarar cafke mutane goma da suka kashe wani mutum tare da kona motoci goma sha daya a kusa da ofishin hukumar zabe ta kasa da ke Uyo babban birnin jihar.

Haka kuma kwamishinan ‘yan’sandan jihar Bashir Makama, ya ce, sun kama wasu mutane da katunan zabe na dindindin da adadinsu ya kai dari da saba’in da tara, sai kuma katin zabe na wucin gadi guda ashirin da bakwai.

Ya ce, yayin samamen sun kama mutane arba’in da daya da suka ce su masu sanya ido ne, sai dai babu wata hujja da ta tabatar da hakan.

Da yake ganawa da manema labarai jiya a garin Uyo Bashir Makama, wanda ya samu wakilcin jami’in yada labaran rundunar ‘yan’sanda jihar ta Akwa Ibom DSP Odiko Ogebeche, ya ce, sun kuma samu nasarar kashe wutar da wadannan bata gari suka kunna.

Sai dai DSP Odiko Ogebece ya musanta cewa rundunar ta kama ‘yan bangan siyasa guda dari hudu da ake cewa sun kama, sai dai ya ce, sun kama mutane goma kuma kawo yanzu babu wanda suka samu yana alaka da wata jam’iyya.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!