Connect with us

Labarai

PENGASSAN ta shiga yajin aiki a fadin Najeriya kan korar ma’aikata sama da 800 a matatar Dangote

Published

on

Kungiyar ma’aikatan manyan jami’an man fetur da iskar gas ta Najeriya, wato PENGASSAN, ta ayyana yajin aiki a fadin kasar, tana zargin matatar man Dangote da korar sama da ma’aikata 800 bisa shiga kungiyar kwadago.

 

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da aka fitar bayan taron gaggawa na majalisar koli ta kungiyar ranar Asabar, 27 ga Satumba, 2025, wacce Sakatare Janar, Lumumba Okugbawa, ya sanya wa hannu.

 

Kungiyar ta umurci mambobinta su daina aiki daga karfe 6 na safe ranar Lahadi, 28 ga Satumba, inda za a fara da addu’o’i na tsawon awa 24. Daga ranar Litinin, 29 ga Satumba, za a fara cikakken yajin aiki a dukkan kamfanonin mai da iskar gas, hukumomi da cibiyoyi a Najeriya.

 

PENGASSAN ta ce babu wani aiki da za a yi a wuraren aiki sai na kare lafiyar ma’aikata ko dukiya, wanda kuma sai da izinin babban ofishin kungiyar.

 

Kungiyar ta kara da cewa matatar ta maye gurbin ma’aikatan da aka kora da ‘yan Indiya fiye da 2,000, lamarin da ta bayyana a matsayin cin fuska ga ‘yan Najeriya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!