Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Wasanni

Principal Cup: Zai magance dogaro ga masu taka leda a ketare

Published

on

Ministan matasa da wasanni Sunday Dare, ya ce matukar aka farfado da gasar cin kofin makarantun sakandire a fadin kasar nan, to ba sai an dogara ga ‘yan wasan Najeriya dake taka leda a kasashen waje ba.

Sunday Dare ya bayyana haka ne a jihar Lagos, yayin taron gabatar da hoton gasar da kuma jagororin da za’a yi amfani da su wajen gudanar da gasar ta wannan shekarar da muke ciki.

Ministan ya ce, “A matsayin sa na minista ya taba shawartar shugaban hukumar kwallon kafa ta kasa Amaju Pinnick da ya taka zuwa kasar Ingila don ya roki dan wasa Bukayo Saka ya bugawa Najeriya wasa”.

Ya kuma ce, idan aka inganta tare da farfado da gasar cin kofin makarantun sakandire tun daga matakin farko, babu bukatar tada jijiyar wuya wajen lallashin wani dan wasa don shigawa tawagar kasar nan.

A nasa bangaren shugaban hukumar NFF Amaju Pinncik, ya ce, “NFF ta shirya tsaf wajen bada duk irin gudunmowar da masu shirya gasar ka iya bukata a ko da yaushe”.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!