Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Rahoton na musamman: kan ranar Damukradiya ta duniya

Published

on

Masana da masu sharhi kan al’amuran dake gudana a Nijeriya sun ce babban kalubalen da kasar tafi fuskanta tun bayan fara gudanar da tsarin mulkin dimukradiyya shine rashin samar da ingantaccen ilimi da kuma bunkasa tattalin arziki.

Wannan na zuwa ne a dai dai lokacin da ake gudanar da bikin ranar dimukradiyya ta duniya a yau.

Bikin ranar dimukradiyya a bana ya zo ne a dai dai lokacin da ‘yan Najeriya ke bukatar cin moriyar dimukradiyyar, ta hanyar samar musu da ingantaccen ilimi da bunkasa fannin lafiya da tsaro da tattalin arziki da kuma kayan more rayuwa.

Wannan dai shine lokaci mafi tsaho da farar hula suka dade suna gudanar da mulki tunda Najeriyar ta samu yancin kai a shekarar 1960.

Tun bayan da farar hula ta karbi mulki, a iya cewa akwai bangarori da dama da aka samu ci gaba da kuma wuraren da aka samu nakasu wanda al’ummar kasar ke fatan shuwagabanni su kawo gyara don su ci moriyar dimukradiyyar.

Majalisar dinkin duniya ce dai ta ware duk ranar 15 ga watan satumbar ko wacce shekara a matsayin ranar dimukradiyya,da nufin karfafawa gwamnatoci gwiwa wajen gudanar da tsari da kuma mulkin dimukradiyya.

Taken bikin ranar a bana dai shine hada kai domin tallafawa a samar da ci gaba a karni na gaba.

Rahoton: Ummulkairi Abubakar Ungoggo

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!