Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

KCSF ta karyata rahoton da yake yawo na dakatar da shugabancin kungiyar

Published

on

Kwamatin amintattuna na gamayyar kungiyoyin kishin al’umma a nan jihar Kano Civil Society Forum, ya ce zai yi duk mai yuwuwa wajen ganin an ci gaba da samun hadin kai tsakanin kungiyoyin kishin al’umma a Jihar.

Hakan na cikin wata sanarwa da sakataren kwamatin, Alhaji Hamisu Isah Sharifai ya fitar ga manema labarai.

Sanarwar ta ce, hakan ya biyo bayan rahotonnin da kwamatin ya samu kan cire shugaban gamayyar kungiyoyin Ibrahim Wayya da wasu ke ikirarin yi.

Ta cikin sanarwar kwamatin ya kuma ce har yanzu shugabannin kungiyar sune halastattun shugabanni.

Sai dai Jim kadan bayan fitar wannan sanarwa shugaban gamayyar kungiyoyin da ake ikirarin cirewa Ibrahim Wayya ya cewa wadanda suka sauke shugabannin basu da hurumin hakan, da suke zargin akwai siyasa a cikin lamarin.

Wayya ya ce kowacce kungiya tana da tsare-tsaren da take bi wajen zaban shugabanninta, da Kuma sauya su, saboda haka wancan rahoton bashi da tushe ko makama.

Rahoton: Abubakar Tijjani Rabi’u

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!