Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Gwamnatin Nijeriya ta Fadi lokacin kammala aikin hanyar dogo ta Kano zuwa Maraɗi

Published

on

Gwamnatin tarayyar Nijeriya ta ce nan da ƙarshen shekarar 2025 zata kammala aikin hanyar dogo da ta tashi daga Kano zuwa Maraɗi da kuma buɗe jami’ar horar da harkar tafiye tafiye dake Daura a ƙarshen shekarar nan domin samin sauki a harkar sufuri a faɗin ƙasar.

Babban ministan sufuri Alhaji Sa’idu Ahmad Alƙali ne ya bayyana hakan a yayin da yake duba aikin haryar domin ganin yadda aikin yake gudana da yadda aka gina jami’ar horar da harkar tafiye tafiyen da kuma yadda za’a mayar da hankali wajen kammala su akan lokaci.

Ministan ya kuma ce ‘muhimmancin aikin yasa yanzu haka gwamnati zata mayar da hankali domin kammala shi da kuma buɗe jami’ar, tare da duba gyare-gyaren da ya kamata ayi kafin bude makarantar’

Da yake jawabi shugaban Jami’ar horar da harkar tafiye tafiye ta Muhammadu Buhari dake Daura Farfesa Umar Adamu Katsal yabawa ziyarar da yakai wannan Jami’ar duk da tarin ayyukan da ke gabanshi, Wanda hakan na nuni da cewa ya dau wannan makarantar da mahimmanci.
Freedom radio ta rawaito cewa ministan ya sami rakiyar manyan ma’aikata domin duba yadda aikin yake gudana.

Rahoton: Umar Abdullahi Sheka

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!