Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Rashawa: Wani bincike ya bayyana Gwamnatin Nijar da yin badaƙalar kwangila

Published

on

Jamhuriyar Nijar ta musanta wani zargi da yace gwamnatin da ta shude ta Mahammadou Issoufou ta bada kwangila ta haramtacciyar hanya.

Wani dan jarida mai binciken ƙwaƙwaf kuma shugaban kungiyar ƴanjaridu na kasashen yammacin Afirca masu binciken ƙwaƙwaf Moussa Aksar, ya bayyawa Freedom Radio cewa sun samu takardu miliyan dubu goma shabiyu sun kuma samu camfanoni da paspo din mutane daga ƙasashen Russia da Nijar, da kuma Senegal, wadanda suka yi kwangila ba bisa ƙa’ida ba tun a shekarar 2007.Sannan suka sake dawo a shekarar 2012, lokacin mulkin Mahammadou Issoufou.

Tunda fari dai, gwamnatin kasar mai ci, ta bakin Ministan ma’adanai Madame Hussaini Hadizatou Yakouba ta musanta wannan sakamakon rahoton, ta kuma ce da tun asali anzo ga gwamnati da an tabbatar da gaskiyar lamarin.

Daga ƙarshe kuma, ta shawarci masu gudanar da bincike irin wannan da su guji yaɗa labarin ƙarya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!