Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Rashin kwararrun malamai ya kawo koma baya a fannin ilimin kimiyya –KASSOSA

Published

on

Kungiyar tsoffin daliban Kwalejojin Kimiyya na jihar Kano da Jigawa KASSOSA ta bayyana damuwarta kan rashin kwararrun malamai a fannin da kuma rashin kayan aiki.

Tsohon shugaban kungiyar daliban kuma shugaban kwamitin gudanar da zaben kungiyar ta KASSOSA Muhammad Ja’afar Na’abba ne ya bayyana hakan, jim kadan bayan kammala shirin Barka da Hantsi, na nan tashar Freedom Radio.

Muhammad Na’abba ya ce, kungiyar na taka muhimmiyar rawa wajen inganta harkokin kimiyya da fasaha a ko wane bangare, sai a yanzu akwai banbanci tsakanin ilimin kimiyya a shekarun baya da kuma yanzu.

Ya ce, rashin na’urorin aiki da kuma rashin kwararrun malamai ya taka rawa wajen tabarbarewar ilimin kimiyya a kasar nan.

Muhammad Na’abba ya yi kira ga iyaye da su rika barin ‘ya’yansu suna zabar fannin da ya kamata su karanta da kansu, domin samun nagartaccen ilimi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!