Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Shari’ar neman hakki na neman gagarar talaka – Barista Badiyya

Published

on

Kungiyar lauyoyi ta kasa reshen jihar Kano ta bayyana fargabar ta kan Karin kudaden cike takardun rantsuwa da na shigar da kara da sauran abubuwan da suka shafi ‘yan sanda.

Barista Badiyya Abdullahi Mua’zu ce ta yi wannan korafi ta cikin shirin ‘yanci da rayuwa na nan Freedom Radio.

Barista Badiyya ta ce abin fargabar ma shine yadda wannan matsala zata iya shafar talaka kai tsaye, ta yadda ba zai iya shigar da kara ba ko da kuwa an zalunce shi.

Barista tace a da ana sayar da takardar ranstuwa ta Affidavit akan naira dari biyu amma a yanzu ya kai naira dubu shida.

Labarai masu alaka:

Rana zafi : Ƴan shara sun shiga yajin aiki a Kaduna

Rashin adalci a shari’a shi ke haifar da matsaloli – KCSF

Ta kuma ce abin takaicin kuma shine babu wata doka da ta bada damar kara wannan adadin kudi da yawa haka.

To sai dai da ya ke mayar da jawabi ta cikin shirin, kakakin babbar kotun jihar Kano Baba Jibo Ibrahim ya ce Karin kudin na nan kunshe cikin kundin doka.

Ya ce su kansu Karin ya tayar musu da hankali, kasancewar idan aka tafi a haka, to kuwa shari’a zata iya gagarar talaka, amma dai abu ne da za’a a iya gyarawa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!