Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Rashin manufa da aƙida ne ke sa ƴan siyasa sauya sheƙa – Farfesa Kamilu Fagge

Published

on

Masanin kimiyyar siyasar nan na Jami’ar Bayero a Kano Farfesa Kamilu Sani Fagge ya ce rashin manufa da aƙida ne ke sanya ƴan siyasa sauya sheƙa a dai dai lokacin da kakar zaɓe ke ci gaba da kankama.

Farfesa Kamilu Sani Fagge ya bayyana hakan jim kaɗan bayan kammala shirin Barka da Hantsi na tashar Freedom Radio.

Farfesa Kamilu Sani Fagge ya ce “A yanzu ana siyasa ne don biyan buƙatar kai hakan ne ya sanya ƴan siyasa a yanzu ke sauya sheƙa daga wata jam’iyya zuwa wata”.

“Babu Aƙidar dumukradiyya a zuciyar ƴan siyasa manufarsu a iya baki take da kuma buƙatar kansu, kuma shi rikicin siyasa na ragewa jam’iyya ƙarfi kuma ya na janyo ƴan jam’iyyar su yi mata ƙafar ungulu” a cewar Fagge

Farfesa Kamilu Sani Fagge ya kuma ce idan har ana son kawo gyara a dumukradiyyar ƙasar nan sai wasu tsirarun mutane sun dai na ɗaukar kansu sune dumukradiyya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!