Labarai
Rashin shugabanci na gari ne cikas ga ci gaban kasashen Afirka- Obasanjo

Tsohon shugaban kasar nan, Cif Olusegun Obasanjo, ya bayyana cewa rashin shugabanci na gari shi ne babban abin da ke kawo cikas ga ci gaban kasashen Afirka.
Cif Olusegun Obasanjo ya bayyana hakan ne a birnin Abeokutan, jihar Ogun, yayin da yake jawabi ga daliban da suka kammala karatu a Cibiyar Shugabanci ta Olusegun Obasanjo.
Ya ce, idan aka samu shugabanni marasa inganci, kasashe kan rarrabu, ana sace dukiyar kasa, yara marasa ilimi sukan kwana da yunwa, sannan matasa masu kyakkyawar makoma sukan yanke kauna.
You must be logged in to post a comment Login