Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Rashin wutar lantarki na janyowa Najeriya asarar Naira tiriliyan 11 a duk shekara– Bankin duniya

Published

on

Bankin duniya ya ce rashin isash-shen wutar lantarki ya janyowa bangaren masana’antu da harkokin kasuwanci a Najeriya, asarar makudan kudade dala biliyan 29 kwatankwacin naira tiriliyan goma sha daya.

A rahoton da bankin na duniya ya fitar a jiya laraba, rahoton ya ce, harkokin kasuwanci da sana’oi a Najeriya suna tabka muguwar asarar sama da naira tiriliyan goma sha daya a duk shekara.

Bankin na duniya ya kuma yi ikirarin cewa Najeriya ce kasa da ta fi yawan adadin jama’a da ba sa samun wutar lantarki a duniya.

Babban jami’in bankin da ke kula da yammaci da tsakiyar afurka, Ashish Khanna, ya ce, rashin wutar na matukar janyo koma baya ga harkokin tattalin arzikin Najeriya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!