Connect with us

Labaran Kano

Rikicin masarautar Kano na dab da warwarewa – Gwamna Yusuf

Published

on

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ce ana samun karuwar fahimtar juna a siyasar jihar, tare da fatan rikicin masarautar Kano zai warware cikin lumana.

Abba Kabir Yusuf ya bayyana haka ne yayin wani taron addu’o’i da karatun Al-Kur’ani a gidan gwamnati, inda mahalarta suka yi addu’ar zaman lafiya da hadin kai.

Gwamnan ya ce halartar Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Barau Jibrin, a wasu taruka alama ce ta ingantuwar dangantaka ta siyasa.

Ya kuma bukaci ‘yan siyasa su guji siyasar gaba da gaba, tare da jaddada kudurin gwamnati na yaki da daba da kuma aiwatar da ayyukan raya jama’a.

A nasa jawabin, Sarkin Kano, Muhammad Sanusi II, ya bukaci al’umma su ci gaba da addu’a domin zaman lafiya da ci gaban jihar da kasa baki daya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!