Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Rikicin shugabanci: Ganduje ya rattaba hannu ga dokar Kantin Kwari

Published

on

Gwamnan Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ya Sanya hannu akan dokar tafiyar da kasuwanci a Kantin kwari, wadda zata tabbatar da gudanar da kasuwancin bisa ka’ida.

Ganduje ya Sanya hannu a dokar ne a yayin zaman majalisar zartarwa a ranar larabar nan, 3 ga watan Nuwanba.

Da yake zantawa da Freedom Radio Kwamishinan Sharia na jihar Kano Barrister Musa Abdullahi Lawan ya ce dokar zata taimaka wajen samarwa gwamnatin jihar kano kudaden shiga da magance rigingimun shugabanci a kasuwar ta Kantin kwari.

A wani labarin kuma, Gwamna Ganduje ya sanya hannu akan dokar da za ta rika tafiyar da ayyukan hukumar yawon bude idanu, inda Kwamishinan na shari’ah ya ce dokar zata taimaka wajen riƙa tafiya da zamani Wanda zai ƙara kawo wa jihar ta kano kudaden shiga

Dr Abdullahi Umar Ganduje ya Kuma sanya hannu akan dokar da aka gyara ta majalisar wayar da kan jamaa wato community reorientation council law amendment

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!