Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Rikicin siyasa : Yadda kotu ta bada umarnin kama shugaban karamar hukuma a Kano

Published

on

Kotun Majistire mai zamanta a garin Gezawa karkashin jagorancin mai sharia’a Salisu Haruna Bala, ta bai wa rundunar ‘yan sandan Jihar Kano umarnin kama shugaban karamar hukumar Gaya Ahmad Tashi Abdullahi da shugaban Kansiloli na Gaya Shu’aibu Mai Gado Gamarya a duk inda suke.

Tunda farko masu neman takarar shugabancin karamar hukumar Gaya guda bakwai ne suka shigar da kara a gaban kotun, sakamakon zargin dukan kawo wuka da suke zargin shugaban karamar hukumar da shugaban kansiloli na Gaya sun yi wa mutane biyu daga cikinsu a wajen tantancewa a ranar laraba 11 ga watan Nuwanban da muke ciki.

A yayin zaman kotun na yau mai shari’a Salisu Haruna Bala ya saurari dukkan bangarorin biyu, bayan kammala sauraron ne kuma nan take ya baiwa DPO na Gaya da na Gezawa umarnin kamo wadanda ake zargi da aikata laifin domin dankawa Kwamishinan ‘yan sanda na Kano, don ci gaba da gudanar da bincike a kan lamarin.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!