Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Za mu soke rijistar kamfani dake satar suna a kasar nan – SON

Published

on

Hukumar kula da ingancin kayayyaki ta kasa SON ta ce ba za ta saurarawa kamfanoni da sauran ‘yan kasuwa masu amfani da jabun kayayyaki da ma sauran kaya marasa inganci a cikin al’ummar kasar nan ba.

Babban daraktan hukumar Malam Faruk Salim ne ya bayyana hakan a yayin wata ziyara daya kai wa kungiyar hadin kai ta kasuwar kasa da kasa dake Alaba a ofishinta dake birnin Ikko.

Malam Faruk Salim Yana mai cewa, sarrafa kayayyakin jabu na cikin abubuwan dake assasa gazawar cika ka’idar hukumar tabbatar da nagartar kamfanoni ta kasa
Inda ya ce hukumar za ta soke rajistar duk wani kamfani ko cibiyar sarrafa kayayyakin da suka yi satar sunan wani don aikata ba daidai ba.

Malam Farouk Sulaiman ya ce lamarin hakkin mallaka ba abu ne da hukumarsa za ta iya yaki da shi ita kadai ba, har sai sauran hukumomin da suke da ruwa da tsaki a fannin sun bada tasu gudunmawar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!