Connect with us

Labarai

Rundunar ƴansandan Kano ta buƙaci jami’anta su tsananta sanya idanu a kan iyakokin jihar

Published

on

 

Rundunar ƴansandan jhar Kano ta buƙaci jami’anta su tsananta sanya idanu a kan iyakokin jihar.

Kwamishin ƴanandan jihar, CP Adamu Bakori ne ya bayyana haka lokacin da ya jagoranci wata tawagar jami’an rundunar zuwa yankunan ƙananan hukumomin Tsanyawa da Shanono da ke kan iyakar jihar da Katsina.

CP Bakori ya buƙaci jami’an tsaron da ke sintiri a yankunan su tsananta sanya idanu da matsin lamba kan miyagun da ke harkokinsu a yankunan domin maido da zaman lafiya.

A baya-bayan nan jihar Kano ta riƙa fuskantar hare-haren ƴanbindiga masu satar mutane domin neman kudin fansa a yankunan jihar da suka yi iyaka da Katsina mai fama da hare-hare.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!