Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Rundunar soja ta mikawa gwamnatin Borno ‘yar Chibok din da suka ceto a baya-baya nan

Published

on

Rundunar sojin kasar nan ta mikawa gwamnatin jihar Borno daya daga cikin daliban makarantar sakandiren Chibok, mai suna Salomi Pogu wadda suka samu nasarar ceto daga hannun mayakan Boko Haram, a baya-bayan nan.

Da yake mika yan matan biyu ga mataimakin gwamnan jihar Usman Durkwa a birnin Maidugurin jihar Borno, kwamandan Operation Lafiya Dole Manjo Janar Rogers Nicholas yace sun samu nasarar ceto Salomi Pogu ranar 4 ga watan Janairu tare da Jamila Adams a garin Pulka da ke yankin karamar hukumar Gwoza.

Mista Nicholas ya kuma bukaci gwamnatin jihar da tayi yan matan biyu rijista, kamar yanda aka yiwa sauran ‘yan matan da aka ceto a baya, kafin mika su hannun iyayen su.

Da yake jawabi, mataimakin gwamnan jihar Borno Usman Durkwa ya yabawa rundunar ta Operation Lafiya dole bisa irin rawar da ta taka wajen ceto ‘yan matan, da kuma irin namijin kokarin da takeyi wajen yakar yan tada kayar bayan.

Usman Durkwa ya bayyana fatan sa na ganin cewar an samu nasarar ceto sauran ‘yan matan da ke hannun ‘yan kungiyar ta Boko Haram.

A shekarar 2014 ne kungiyar ta Boko Haram ta sace yan matan sakandiren Chibok su dari biyu da goma sha tara.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!