Labarai
Rundunar soji ta tabbatar da rahoton tashin Bom a bakin barikin Mogadishu

Sojojin a birnin tarayya Abuja sun tabbatar da rahoton samun fashewar wani abu a kusa da barikin soji a birnin na Abuja.
Lamarin ya faru ne a barikin sojoji na Mogadishu da ke kan hanyar Mararaba-Nyanya.
Rahotonni sun bayyana cewa, wanda ya tayar da bam ɗin ya mutu, yayin da aka samu jikkatar mutum guda inda yanzu haka ya ke samun kulawa a asibitin sojojin.
Sojojin sun ce an shawo kan lamarin zuwa yanzu, tare da cewa babu wata fargaba don haka mutane su kwantar da hankalinsu.
You must be logged in to post a comment Login