Connect with us

Labarai

Rundunar sojin sama a Najeriya sun kashe ‘yan fashin daji a jihar Zamfara

Published

on

Rundunar sojan sama ta Najeriya ta ce ta yi nasarar kashe ‘yanfashi da dama a garin Tsafe na jihar Zamfara bayan yi musu kwantan bauna ta hanyar amfani da jiragen yaki ta sama.

 

Mai magana da yawun rundunar,,Air Commodore Ehimen Ejodame, ya ce an kai hare-haren ne kan sansanin ‘yanfashin a  ranar Juma’a 14 ga watan Nuwamba 2025 bayan tattara bayanan siri da suka samu.

 

Ya ce bayanai sun tabbatar da ‘yanbindigar na karakaina a wurin da suka ɓoye shanun sata da ke kan wani tsauni da ke ba su kariya da kuma ajiye kayayyaki.

 

“An kai hare-hare da dama waɗanda suka dira kan ‘yanfashin da ke yunƙurin guduwa cikin duhun daji, inda aka bi su kuma aka kashe su,” in ji sanarwar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!