Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Kaciyar da ake yiwa mata na haifar musu matsaloli yayin haihuwa-Dr. Zainab Datti

Published

on

Wata kwararriyar Likita a bangaren Cututtukan da suka shafi mata, Dokta Zainab Datti Ahmad, ta bayyana cewa shayi da ake wa ‘ya’ya mata na daya daga cikin babban kalubalen da ke haifarwa mata matsaloli yayin haihuwa.

Dakta Zainab Datti Ahmed wadda Likita ce a Asibitin koyarwa na Aminu Kano, ta bayyana hakan ne yayin zantawa da ita jim kadan bayan kammala shirin Barka da Hantsi na nan Freedom Rediyo, a wani bangare na bikin yaki da yiwa ‘ya’ya mata kaciya  da ake gudanarwa a Talatar nan.

Kwarariyar likitar ta kara da cewa matan da aka yiwa shayin na kamuwa da wasu cutuka da suka shafi zubar da jini da matsanincin ciwon mara.

Dokta Zainab Datti Ahmad ta ce kamata ya yi gwamnati ta kara kaimi wajen kirkiro shirye-shiryen da za su rika wayar da kan mutane dangane da illolin da ke tattare da yi wa ‘ya’ya mata shayi .

Zainab Ahmed ta kuma shawarci iyaye da su guji yiwa ‘ya’yan su mata kaciya  don magance matsalolin da suke samu yayin zamantakewar aure.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!