Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Rundunar ‘yan sanda zata aika jirage yankunan da ake rikici

Published

on

Sufeto Janar na ‘yan sandan Nageriya Muhammad Adamu, ya ba da umarnin turawa da jirage masu saukar ungulu na rundunar a sassan kasar baki daya domin dakile matsalolin tsaro.

Rahotanni sun ce, jiragen na shalkwabta zasu gudanar da aiki a sassan kudu maso yammaci da kuma arewa maso yammacin kasar .

Hakan na  kunshe ne cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun jami’in yada labaran rundunar, DCP Frank Mba.

Sanarwar ta ce jiragen masu saukar ungulu zasu rika kula da harkokin tsaro a yankunan arewa maso yammaci da kuma kudu maso yammaci wanda nan ne aka fi samun matsalolin ayyukan batagari a wannan lokacin.

A cewar sanarwar, akwai cibiya a Abuja da za ta rika kula da titin Kaduna zuwa Abuja da kuma sauran jihohi da ke yankunan arewa maso tsakiya da arewa maso yamma, sai kuma cibiyar da ke jihar Ondo wadda za ta rika kula da jihohin kudu maso yammci.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!