Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Tsaro

Rundunar yan sandan Kano ta shirya yin gwajin kayan aikin tsaro

Published

on

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta ce, da misalin karfe 12:00 na ranar gobe Lahadi za ta gudanar da wani Atisayen nuna karfin kayayyakin aikin kwantar da tarzoma da rundunar ke da su domin a jiye su a guraren da aka tsara.

 

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Muhammad Hussain Gumel, ne ya bayyana hakan yayin zantawa da manema labarai da yammacin yau Asabar.

 

Muhammad Gumel ya ce, ba wai suna so su tsorata mutane ba ne yayin Atisayen da zasu gudanar, kawai dai za su yi hakan ne domin ya zama gargadi da jankunne ga masu kokarin tayar da fitina a Kano.

 

A cewarsa babu wani mahaluki da rundunar ‘yan sandan Kano za ta saurara wa matukar ya yi yunkurin tayar da husuma a zabe ko kuma bayan fitar da sakamako.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!