Connect with us

Labarai

Rundunar ‘yan sandan Zamfara ta tabbatar da mutuwar makiyaya 15 a harin Bawon Daji

Published

on

Rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara ta tabbatar da mutuwar makiyaya goma sha biyar a jihar.

Mai magana da yawun rundunar, Muhammad Shehu, ya shaidawa manema labarai cewa, ‘yan bindigar sun kai harin ne a kauyen Bawon-Daji da ke karamar hukumar Anka.

A cewar sa,shugaban karamar hukumar Anka Alhaji Mustapha Gado Anka ya shaida musu cewa, ‘yan bindigar sun je kauyen ne akan babura da misalin karfe 1:00pm, inda suka bude wuta kan mai uwa da wabi, kafin daga bisani suka tsere zuwa cikin dajin da ke makwabtaka da kauyen.

Ko a baya-bayan nan ma ‘yan bindigar sun kai hari a jihar ta Zamfara inda suka kashe mutane da dama.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!