Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Addini

Sabuwar Shekarar Musulunci: Ganduje ya ayyana litinin a matsayin ranar hutu ga ma’aikata

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta ayyana ranar Litinin 09 ga watan Agustan 2021 a matsayin ranar hutu ga ma’aikata don murnar shigowar sabuwar shekarar Musulunci

Gwamna Dakta Abdullahi Umar Ganduje ne ya ayyana Litinin din, da ke zaman 1 ga watan Muharram hijra 1443.

Gwamnan ya bayyana hakan ta cikin sanarwar da kwamishinan yada labarai Malam Muhammad Garba ya sanya wa hannu.

Sanarwar ta bayyana cewa, hutun wani bangare ne na tunawa da sabuwar kalandar Musulunci ta 1443, a don haka an bukaci ma’aikata da su yi amfani da ranar wajen gudanar da addu’o’in neman zaman lafiya a kasar nan.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!