Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Sai gwamnatin Najeriya ta zuba jarin Dala biliyan 10 za ta iya farfaɗo da harkokin lantarki- Adebayo

Published

on

Ministan Wutar Lantarki, Adebayo Adelabu ya ce Gwamnatin Tarayya na bukatar zuba jarin dala biliyan 10 a duk shekara, domin farfado da harkar wutar lantarki na tsawon shekaru 10 masu zuwa.

Ministan  ya bayyana haka ne a birnin Tarayya Abuja,  ya yin  wani taron  zaman bincike na kwana daya kan kudurin dakatar da karin kudin wutar lantarki da hukumar kula da wutar lantarki ta kasa  (NERC) ta yi, da Majalisar Dattawa ta bukaci a yi Binciken.

A cewar Adelabu,  gwamnati na bukatar kashe kasa da dala biliyan 10 a duk shekara nan da shekaru 10 masu zuwa, muddin ana bukatar samar da tsayayyar wutar Lantarki a fadin kasar.

A cewar sa Hakan ya biyo bayan abubuwan da ake bukata na samar da ingantaccen kayan aiki a fannin, amma gwamnati ba za ta iya daukar nauyin hakan ba.

Inda ya kara dacewa dole ne Gwamnati  ta sanya fannin ya zama a bude  ga masu zuba jari da masu ba da lamuni, don cimma manufar da aka sa a gaba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!