Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Sama da mutane 10 sun rasa ransu sakamakon hatsarin mota a Kwara

Published

on

Hukumar kiyaye afkuwar hadura ta kasa (FRSC) ta ce mutum 10 sun rasa ransu a ranar Talata 20 ga watan Yuli a jihar Kwara sakamakon afkuwar wani mummunan hatsari mota.

Shugaban hukumar a jihar Jonathan Owoade ne ya bayyana hakan ga manema labarai.

Ya kuma ce, hatsarin ya afku ne a yankin Olooru-Okolowo a kan titin Ilorin-Jebba dake karamar hukumar Moro a jihar sakamakon gudun wuce sa’a da direban motar keyi.

Hukumar ta kuma ja kunnan direbobi da su guji gudun wuce sa’a a abubuwan hawa musamman a wannan lokaci da ake gudanar da bukukuwan sallah.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!