Labarai
Samar da yan sandan jihohi zai kawo karshen matsalar tsaro –ALGON
![](https://freedomradionig.com/wp-content/uploads/2021/03/51b8d7898438f.image_.jpg)
Shugaban kungiyar kananan hukumomin Najeriya ALGON, Kolade Alabi, ya sake nanata bukatar samar da ‘yan sandan jihohi.
Shugaban yayi wannan kira ne lokacin da ya jagoranci kwamitin zartarwa na kungiyar a wata ziyarar jaje da suka kai wa gwamnan jihar Naija Abubakar Sani Bello.
A cewar Alabi, za a iya shawo kan kalubalen tsaro a yanzu idan aka samar da ‘yan sandan jihohi a kasar nan, domin kuwa za su iya kawo karshen ayyukan yan tada kayar baya a yankunan su.
Alabi ya yi kira da a kara wa jihohi da kananan hukumomi kaso don magance kalubalen abubuwan more rayuwa da kuma gazawar tsaro
You must be logged in to post a comment Login