Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Kowanne banki ya gabatar da kadarorin sa kafin watan Yuni – EFCC

Published

on

Hukumar da ke yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa, EFCC, ta bukaci masu harkar hada-hadar kudi a Najeriya musamman masu bankuna da su bayyana kadarorinsu ga hukumar kafin wa’adin daya ga watan Yuni mai zuwa.

Shugaban Hukumar, Abdulrashed Bawa ne ya fadi wannan bayanin a ranar Talata yayin da yake zantawa da manema labarai a fadar shugaban kasa jimmkadan bayan kammala ganawa da shugaba Muhammadu Buhari.

Wannan dai na cikin wata sanarwa da mai taimakawa shugabn hukumar kan al’amuran yada labarai licity Wilson Uwujaren ya fitar, na bayyana cewa matakin ya biyo bayan tantance ayyukan ma’aikatan Banki da sauran al’amuran da suka shafi kudi karkashin dokar bayyana kadarori ta shekarar 1986.

A cewar sanarwar sashi na 1 na ma’aikatan Bankin da al’amuran kudi ta tilasta kowane ma’aikacin Banki da ya yi cikakken bayani game da kadarorin da ya mallaka lokacin aiki, da kuma duk shekara.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!