Labarai
Sanatoci sun fitar da sunan sabon shugaban babban bankin CBN
![](https://freedomradionig.com/wp-content/uploads/2023/09/IMG_20230926_221942.jpg)
Majalisar dattawa ta tabbatar da Olayemi Cardoso a matsayin gwamnan babban bankin Nijeriya CBN.
Shugaban Majalisar ne ya bayyana hakan yayin zaman da majalisar tayi don tantance wadanda suka cancanta a matsayin shugaban babban bankin, da mataimakansa a yau.
Haka zalika majalisar ta tabbatar da mutane hudu a matsayin mataimakan gwamnan da suka hadar da Emem Nnana Usoro da Muhammad Sani Abdullahi Dattijo da Philip Ikeazor da Kuma Bala Bello.
You must be logged in to post a comment Login